Isa ga babban shafi
Wasanni

Dubban matan Iran sun nuna maitarsu kan kwallon kafa

Dubban ‘yan matan Iran sun yi tururuwar saye tikitin kallon wasan da kasar za ta yi da Cambodia a birnin Tehran a gobe Alhamis a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2022.

'Yan matan Iran masoya kwallon kafa
'Yan matan Iran masoya kwallon kafa Reuters
Talla

Wannan na zuwa ne bayan hukumomin Iran sun tabbatar wa Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya, FIFA cewa, a wannan karo za su amince wa mata shiga fili domin kallon wasa kai tsaye, yayin da aka ware bangaren da mata zalla za su zauna a filin na Tehran.

Hukumomin Iran sun ce, cikin ‘yan mintoci kalilan, matan suka saye daukacin tikiti dubu 3 da 500 da aka ware musu a shafin intanet.

Kimanin shekaru 40 kenn da Iran ta haramta wa mata shiga filin wasa kwallon kafa bisa dalilai na addinin Islama.

Sai dai a watan jiya Hukumar FIFA ta umarci Iran da ta bude kofa ga matan domin shiga filayen wasanni biyo bayan mutuwar wata matashiya da aka cafke ta a lokacin da take kokarin shiga fili bayan ta yi shigar maza.

Matshiyar da ake yi wa lakabi da Blue Girl ta cinna wa kanta wuta har lahira saboda fargabar fuskantar hukuncin dauri a gidan yari

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.