Isa ga babban shafi
wasanni

"Argentina za ta doke Najeriya a Rasha"

Tsohon kocin Argentina da ya jagoranci kasar wajen lashe kofin duniya a shekarar 1978 Luis Menotti ya ce, kai tsaye tawagar kasar za ta samu maki uku a rukunin da ta fada a gasar cin kofin duniya da za a gudanar a Rasha a badi.

'Yan wasan Najeriya sun casa Argentina da ci 4-2 a wasan sada zumunci a cikin watan jiya
'Yan wasan Najeriya sun casa Argentina da ci 4-2 a wasan sada zumunci a cikin watan jiya PIUS UTOMI EKPEI / AFP
Talla

Argentina na cikin rukuni guda da Najeriya, kuma a ranar 26 ga watan Junin 2018 ne kasashen biyu za su fafata a Rasha.

Tarihi ya nuna cewa, sau hudu Argentina da Najeriya suka hadu a matakin rukuni a gasar cin kofin duniya, kuma Argentiana ce ke samun nasara akan Najeriya da banbacin kwallo guda.

Tsohon kocin ya ce, ba zai yi mamaki ba idan Croatia ta casa Argentina amma a cewarsa, babu shakka kasar za ta samu maki akan Iceland da Najeriya a mataki rukuninsu na D.

A cikin watan jiya ne, Najeriya ta doke Argentina da ci 4-2 a wasan sada zumunta amma masharhanta na cewa, wannan ba wani abu bane idan aka kwatanta da fafatawar da za su yi a gasar cin kofin duniya a Rasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.