Neymar na Brazil ba zai bar Santos ba sai zuwa 2014
Neymar Matashin dan wasan Brazil wanda zai yi bukin cika shekaru 20 a watan gobe, yace zai ci gaba da rayuwarsa a kungiyar shi ta Santos har zuwa watan Yulin shekarar 2014, bayan kammala gasar cin kofin Duniya a Brazil.
Wallafawa ranar:
Neymar ya bayyana haka ne lokacin da ya kai ziyara Montevideo babban birnin kasar Uruguay, domin karbar kyautar gwarzon dan wasan yankin Amurka.
A cewar Neymar ba zai bar Santos ba har sai kwangilar shi ta kawo karshe da Santos a shekarar 2014 bayan sabunta kwangilar a watan Nuwamban bara.
Neymar ya zira yawan kwallaye 81 cikin wasannu 159 daya buga a Santos.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu