Isa ga babban shafi
Faransa

Faransawa na zaben sabon shugaban kasa

Faransawa na gudanar da zaben shugaban kasa zagaye na biyu inda za su zabi sabon shugaba tsakanin ‘yan takara biyu Marine Le Pen da kuma Emmanuel Macron da ke fafatawa a zaben a yau Lahadi

Emmanuel Macron da Marine Le Pen yan takarar shugaban kasa a Faransa
Emmanuel Macron da Marine Le Pen yan takarar shugaban kasa a Faransa RFI
Talla

Zaben dai ya yi matukar daukar hankulan kasashen duniya, lura da irin bamabancin manufofi da ke tsakanin yan takarar biyu.

Sai dai an samu karancin rashin fitowar masu kada kuri’a a zaben na yau da ke dab da kammalawa cikin tsauraran matakan tsaro

Abdoulkarim Ibrahim Shikal da ke sa ido a zaben a Paris fadar gwamnatin kasar ya ce kashi 35 suka fito kada kuri’ar a zaben zagayen na biyu.

Zaben shugaban kasar zagaye na biyu da ake gudanarwa a Faransa ya fado ne a lokacin da Faransawa ke hutun karshen mako na kwanaki uku.

Wannan ne karon farko a shekaru 60 da ake gudanar da zaben zagaye na biyu ba tare da ‘yan takarar manyan jam’iyyun siyasar kasar guda biyu ba.

Emmanuel Macron, na kada kuri'arsa
Emmanuel Macron, na kada kuri'arsa REUTERS/Philippe Wojazer

Kuma a bana ana fafatawa ne tsakanin ‘yan takara Marine Le Pen mai tsattsauran ra’ayi da kuma Emmanuel Macron mai sassaucin ra’ayi.

Sakamakon kuri’un jin ra’ayin jama’a da aka gudanar kafin zaben sun nuna cewa mutane 7 cikin 10 na masu kada kuri’a ba su da ra’ayin ‘yan takarar guda biyu

Muhimmacin zaben Faransa

Zaben dai nada matukar tasiri ga makomar Tarayyar Turai, lura da girman Faransa a matsayin ta biyu ga karfin tattalin arzikin nahiyar da kuma karfin soji da fada aji a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.

Zaben kuma ana fafatawa ne tsakanin ‘yan takara da manufofinsu suka yi hannun riga da juna, wato tsakanin mai da’awar Tarayyar Turai da kuma mai adawa da kungiyar.

Samun nasarar Le Pen babbar baraka ce ga Tarayyar Turai musamman a daidai lokacin da Birtaniya ke shirin ficewa kungiyar da kuma sauyin da aka samu a Amurka na zaben Donald Trump, bako a siyayar duniya.

Marine Le Pen na kada kuri'arta
Marine Le Pen na kada kuri'arta REUTERS/Charles Platiau

Ana dai sa ran samun sakamakon farko na zaben da misalin karfe 7 agogon GMT bayan kammala kada kuri’a.

A ranar 14 ga Mayu ake sa ran rantsar da duk wanda ya lashe zaben tsakanin Emmanuel Macron ko Marine Le Pen.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.