Isa ga babban shafi
Jamus

An baiwa 'yan gudun hijira da suka je Jamus tsare tsare zama a birnin Berlin

Yau Laraba wasu jaridun kasar Jamus suka buga wasu jerin tsare tsaren zama, ga ‘yan gudun hijiran dake zaune a Berlin, babban birnin kasar. Dama dai kafaffen yada labarun Jamus sun bayyana goyon bayansu ga matakin da mahukuntan kasar suka dauka, na dube kofofi ga ‘yan gudun hijira dake tserewa yake yaken da ake yi a Syria da Iraqi. 

Jamusawa, lokacin da suke karbar 'yan gudun hijira z da suka isa kasar
Jamusawa, lokacin da suke karbar 'yan gudun hijira z da suka isa kasar Reuters/路透社
Talla

Jaridun Bild da BZ ne suka wallafa jerin tsare tsaren, masu shafuka 4, da aka rubuta cikin harshen Larabci, da kuma suka yiwa taken Maraba da zuwa Berlin.
Tsare tsaren, masu shafuka 4, sun kunshi taswirar dake dauke da fassarar sunayen muhimman yankunan birnin, da matsugunan ‘yan gudun hijira da sauran ofisoshin jami’an shige da ficen jama’a.
Tsare tsaren da aka buga a jaridun na yankin Berlin, sun kuma kunshi Kamus na muhimman jumlolin harshen Jamusanci, gaishe gaishe da ranakun mako.
Jaridar BZ ta nemi masu karatu su bayar da bugun na yau laraba, a masayin kyata ga ‘yan gudun hijira, bayan sun gama karantu.
Dama a baya bayan nan Bild, da tafi kowacce jarida kasuwa a Jamus, tayi ta yin wani gangamin da ta kira MUNA TAIMAKAWA, dake kokarin wayar da kanun ‘yan kasar su karbi ‘yan gudun hijiran.
Jamus, da tafi kowacce kasa karfin tattalin arziki a nahiyar Turai, na sa ran karbar masu neman mafaka, su fiye da 800,000, cikin wannan shekarar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.