‘Yan ta’adda sun yi barazanar kashe fasinjojin da suka sace a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 20:50
Shirin ‘Mu Zagaya Duniya’ na wannan makon ya waiwayi lamurra da dama da suka auku a makon da ya kare, cikinsu har da yadda ‘yan ta’adda suka saki bidiyon da a cikinsa suka yi barazanar kashe ilahirin fasinjojin jirgin kasan da suka sace akan hanyar Abuja zuwa Kaduna, sa’o’i bayan harin kwanton baunar da ‘yan bindigar suka yi wa dakarun Najeriya a kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari.
A Iraqi kuwa majalisar dinkin duniya ce ta bayyana cewa daruruwan kananan yara sun rasa rayukansu sakamakon fashewa bama-baman da ake binnewa a gefen hanya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu