'Yan bindiga sun kashe dimbim mutane a Burkina Faso da Mali
Wallafawa ranar:
Kunna - 20:19
Cikin shirin za a ji Yadda sojojin Burkina Faso da na Mali da dama suka rasa rayukansu yayin fafatawa da ‘yan ta’adda da suka kai hare-hare a sassan kasashen biyu.Sai kuma ganawar da aka yi tsakanin Najeriya da Nijar akan hauhawar adadin ‘yan gudun hijirar da ke tserewa daga yankunansu a jihohin Sokoto, katsina da kuma Zamfara, wadanda ke cigaba da kwarara zuwa Jamhuriyar ta Nijar.
A Nahiyar Turai kuwa, Rasha ce ta yi gargadin cewa muddin kasashen Turai da Amurka suka ci gaba da lafta mata takunkuman karya tattalin arziki saboda mamaye Ukraine da ta yi, to fa kowa zai ji a jikinsa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu