Isa ga babban shafi

NRC ta musanta zargin satar taragan jirgi da aka yi wa manbobinta a Borno

Cacar baka ta barke tsakanin gwamnatin Jihar Borno da kungiyar ma’aikatan sufurin jiragen kasa ta  Najeriya, bayan da ‘yan sanda suka kame wasu manbobinta a bisa zargin cewa barayi ne da suka yi yunkurin awon gaba da wasu taragan jirgin kasa. 

Taragan jirgin kasan da ma'aikatan hukummar NRC suka yi kokarin kwashewa daga Maiduguri.
Taragan jirgin kasan da ma'aikatan hukummar NRC suka yi kokarin kwashewa daga Maiduguri. © Borno State Government
Talla

A ranar Asabar din da ta gabata ‘yan sandan jihar Borno suka cafke wasu jami’an hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya NRC bisa zarginsu da yunkurin sace taragan jirgin kasa.

Yayin bayyana bacin ransa kan lamarin Innocent Luka Ajiji shugaban kungiyar ma'aikatan na NRC, ya ce babu gaskiya kan tuhumar da ake yi wa manbobin nasu.  

00:31

Shugaban kungiyar ma'aikatan kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya Innocent Luka Ajiji

Wasu 'yan Borno yayin zanga-zangar neman hana kwashe taragan jirgin kasa a Maiduguri.
Wasu 'yan Borno yayin zanga-zangar neman hana kwashe taragan jirgin kasa a Maiduguri. © Borno State Government

Sai dai mataimakin gwamnan jihar Borno Umar Usman Kadafur, ya musanta zargin da kungiyar ma’aikatan jiragen kasan Najeriyar ke musu, inda ya kara da cewar, matakin hana daukar taragan jirgin kasan da  suka dauka ya biyo bayan zanga-zangar da mutane suka yi kan adawa da kwashe taragan.

00:53

Matiamakin Gwamnan Jihar Borno Umar Usman Kadafur

Kungiyar ma’aikatan kula da sufurin jiragen kasan ta Najeriya dai ta yi gargadin cewa za ta dakatar da ayyukanta, muddin ba a gaggauta sakin ma’aikatan nata da aka kama ba bisa ka’ida ba. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.