Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojin Najeriya ta saki tubabun Mayakan Boko Haram 244

Rundunar sojin Najeriya ta mikawa Gwamnatin jihar Borno mayakan Boko Haram 244 da suka tuba, cikinsu akwai mata 56 da maza 118 sai kuma kananan yara 51.

Babban Hafsan Sojin Najeriya Tukur Yusuf Buratai
Babban Hafsan Sojin Najeriya Tukur Yusuf Buratai AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Shugaban rundunar operation lafiya dole a Borno, Manjo Janar Rogers Nicholas, ya ce sun saki mayakan da suka tuba ne karkashin amincewar Babban hafsan sojin kasar Laftanar Janar Tukur Buratai.

Rogers ya ce sun yi bincike da tantace mutane domin tabbatar da cewa babu wata alaka da ta saura tsakaninsu da Boko Haram.

A lokacin karbansu, Gwamnan Jihar Borno Kashim Shettima ya yabi kokarin da sojin Najeriya ke yi a tsawon shekaru 9 domin murkushe mayakan da kuma alkawarta sada tubabun mayakan da iyalansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.