Najeriya
Rashawa: Gwamnatin Najeriya za ta daure alkalai
Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin daure alkalan da suka azurta kan su da kudaden cin hanci da rashawa tare da kwace kadarorinsu da suka saya da kudaden.
Wallafawa ranar:
Talla
Ministan shari’a Abubakar Malami ne ya bayyana haka a birnin Lagos wajen kaddamar da rahotan kungiyar kare hakkin bil-adama ta SERAP, inda ya ke cewa ya zama wajibi alkalai su tsayar da gaskiya a koda yasuhe.
Malami ya ce gwamnatin Muhammadu Buhari za ta yi iya bakin kokarinta dan hukunta duk wani alkali da aka samu da laifin karbar cin hanci ko kuma azurta kan sa ta hanyar da ba ta kamata ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu