Najeriya na neman taimakon kasashen Duniya
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana kokarin da yake na yaki da cin hanci da rashawa inda ya bukaci taimakon kasashen duniya wajen mayarwa kasar kudaden da aka sace aka kuma jibge a bankunan su.
Wallafawa ranar:
Shugaban Najeriya Buhari na daga cikin shugabanin kasashen duniya na farko da suka yi jawabi a rana ta farko a zaman Majalisar Dinkin Duniya,wanda kuma ya sake jaddada aniyar sa ta murkushe kungiyar boko haram da ceto daliban matan Chibok da ran su, da neman ganin kasashen duniya sun taimakawa Falasdinawa kan halin kuncin da suke ciki.
Dakarun Najeriya na ci gaba da sa kai tareda samun nasara a yaki da suke da kungiyar Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu