Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojojin Najeriya sun kame masu tallafawa Boko Haram

Rundunar Sojin Najeriya shiya ta 25 a Maiduguri Jihar Borno ta bayyana kame wasu mutane 30 da ke tallafawa Mayakan Boko Haram da Abinci a yankin Damboa, kamar yadda kakakin rundunar Kanal Usman Kukasheka ya tattabar wa RFI Hausa.

Tankunan Yaki da Dakarun Najeriya suka kwato daga hannun Mayakan Boko Haram
Tankunan Yaki da Dakarun Najeriya suka kwato daga hannun Mayakan Boko Haram REUTERS
Talla

Kukasheka ya ce an kama mutanen dauke da abinci da dama a Korode da za su kai wa mayakan Boko Haram a yankin Damboa zuwa Azir Wajikoro cikin Jihar Borno.

Mutanen da aka cafke sun ce su ‘Yan kasuwa ne ammasun tabbatar da cewa suna kai wa ‘Yan Boko Haram abinci, a cewar Kukasheka.

Dakarun Najeriya dai na samun galaba akan Boko Haram, kamar yadda shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya tabbatar a lokacin da ya ke ziyara a Ghana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.