Boko Haram ta rasa sakewa a yanzu
Rundunar Sojin Saman Najeriya ta bayyana cewa Mayakan Boko Haram ba ta da sakewa a yanzu har su samu damar kashe mutane ko kuma karbe sansanonin Sojoji.
Wallafawa ranar:
Babban hafson rundunar ne, Saddique Abubakar ya fadi haka a lokacin da yake gabatar da jawabi a wani taro da aka shirya a babban birnin Abuja.
Abubakar ya kara da cewa rundunar Sojin saman ta yi matukar karya lagwan mayakan na Boko Haram a Arewa maso gabashin Kasar.
Shugaban Kasar dai Muhammadu Buhari ya yi alkawarin kawo karshen kungiyar wadda ta salwantar da rayukan al-umma da dama a Najeriya da kasashen dake da makwabtaka da ita da suka hada da Nijar da Kamaru da Chadi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu