Isa ga babban shafi

Shiri na musamman a kan ambaliya

Kamar sauran kasashen duniya, nahiyar Afrika na fama da ambaliyar ruwa irin wadda ba ta taba gani ba a tarihi, wadda ta lalata gidaje da gonaki.

Yadda ambaliyar ruwa ta mamaye wasu yankunan Najeriya
Yadda ambaliyar ruwa ta mamaye wasu yankunan Najeriya © REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Ambaliyar ta yi sanadin mutuwar sama da mutane 160 a jihar Jigawa ta Najeriya, da wasu gwammai a karin jihohi 13 da Chadi.

Miliyoyin mutane ne wannan lamari ya shafa kai tsaye ko kuma akasin haka, sakamakon sauyin yanayi.

Menene ya haddasa wannan ambaliyar ruwa? Me zai kasance tasirinsa a kan tattalin arziki, lafiya da noma? Me za mu iya yi a namu matakin don yaki da sauyin yanayi?

Kasashen da suka ci gaba ne ke da alhakin fitar da kashi 80 na gurbatacciyar iska mai lalata muhalli. Ko akwai wata hanya da za a iya bi wajen tafiyar da ayyukan masana’antu a kasashen nan?

Sashen Hausa na RFI zai sadaukar da wani shiri na musamman a yau da maraice, karfe 4 agogon TU da Ghana, ko kuma karfe 5 agogon Najeriya, Nijar Kamaru da Chadi, inda za mu tattauna wannan lamari na ambaliya tare da amsa tambayoyinku. Za kuma mu ba ku damar tofa albarkacin bakinku a kan wannan maudu’i. Kuna iya kama mu a gajeren zango, ko kuma ta manhajar RFI Pure radio.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.