Isa ga babban shafi

Kasar Congo ta dage jerin takunkuman hana yaduwar cutar ta Covid-19

Hukumomin Congo sun ba da sanarwa a jiya asabar cewa an kawo sassauci tare da dage jerin takunkuman hana yaduwar cutar ta Covid-19, wacce ta kashe kusan mutane 400 a kasar tsakanin shekarar 2020 zuwa 2022.

 Denis Sassou Nguesso.Shugaban  kasar Congo-Brazzaville
Denis Sassou Nguesso.Shugaban kasar Congo-Brazzaville REUTERS/Anis Mili/Files
Talla

Kwamitin daidaito da ke yaƙar cutar ta Covid-19 ya yanke shawarar soke dokar ta-baci bangaren kiwon  lafiya, wacce  aka kaddamar da ita tun  a watan  Maris  na shekara ta 2020, a duk faɗin ƙasar, da kuma ƙarshen sanya kyalen rufe hantsi da baki.

Bugu da kari, ba a bukatar gabatar da sheidar gwajin cewa ba a dauke da kwayar cutar ta Covid 19.

Kwamitin daidaito wanda shugaban kasar Denis Sassou Nguesso ya jagoranta ya yanke shawarar kawo karshen bukatar ma'aikatan lafiya a wasu yankunan kasar ta Congo Brazzaville.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.