Isa ga babban shafi
Congo

Congo Brazzaville na zaben raba gardama

Al’ummar Congo Brazzaville na zaben raba gardama a yau Lahadi faslata kundin tsarin mulki domin amincewa da kudirin shugaban kasar Denis Sassou Nguesso na neman wa’adin shugabanci na uku.

Shugaban Congo Brazzaville Denis-Sassou Nguesso,
Shugaban Congo Brazzaville Denis-Sassou Nguesso, AFP/Thierry Carlier
Talla

An shafe kwanaki ana zanga-zanga a Congo Brazzaville domin nuna adawa da matakin shugaban kasar na yin tazarce.

‘Yan adawa sun ce akalla mutane 20 suka mutu a zanga-zangar.

Shugaba Sassou Nguesso mai shekaru 71 na son ya gyara kundin tsarin mulkin kasar ne domin samun damar tazarce a zaben da da za a gudanar a badi.

A tsarin dokar kasar, an kayyade shekarun dan takarar shugaban kasa zuwa shekaru 70, sannan an kayyade wa’adin shugabanci zuwa biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.