Isa ga babban shafi
Congo Brazaville

‘Yan Sanda sun hallaka masu zanga-zanga a Congo

‘Yan Sanda a Jamhuriyar Demokradiyar Congo sun harbe wasu mutane uku cikin masu zanga-zangar adawa da gwamanatin da suka fantsama a kewayen birnin Kasar.

Masu zanga zanga da ke arangama da 'Yan sanda a Congo Brazaville
Masu zanga zanga da ke arangama da 'Yan sanda a Congo Brazaville AFP PHOTO / Dubourthoumieu Gwenn
Talla

Wani shaidan gani da ido ya bayyana cewa ‘Yan sanda sun bude wuta a kan masu zanga zangar, lamarin da ya yi szanadiyar mutuwar mutanen da ya hada da abokinsa.

Har ila yau mutane 8 sun samu rauni sakamakon rikicin da ya barke tsakanin Jami’an tsaron da masu zanga zangar adawa da yunkurin shugaban kasar, Denis Sassou Nguesso na tsawaita zaman sa a kan karagar mulki bayan ya shafe shekaru da dama a kai.

Wata majiyar kiwon lafiya ta ce, a halin yanzu mutane 7 na kwance a asibitin Makelekele da ke babban birnin kasar ta Jamhuriyar Congo kuma 5 daga cikin su na fama da munanan rauni na harbin bindiga.

A yau ne dai hukumomin kasar suka haramta gudanar da zanga-zangar bayan ‘yan adawa sun bukaci a gudanar da ita .
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.