Isa ga babban shafi
Congo

Za a yi kuri'ar raba gardama kan sabon kundin tsarin mulki a Congo Brazzaville.

Shugaban Congo Brazaville Denis Sasso Nguesso ya ce za a gudanar da kuri’ar raba gardama a kasar domin canza kundin tsarin mulkin kasar wanda hakan zai ba shi damar sake tsayawa takara a zaben shugabacin kasar.

Shugaban Congo-Brazzaville, Denis Sassou-Nguesso.
Shugaban Congo-Brazzaville, Denis Sassou-Nguesso. AFP PHOTO / THIERRY CHARLIER
Talla

Nguesso, mai shekaru 72 a duniya, ya share tsawon shekaru 31 kan karagar mulki, kuma ba ya da izinin tsayawa takara a zaben na shekara mai zuwa.

To sai dai masu hamayya da shi a fagen siyasa sun nuna rashin amincewarsu da hakan, yayin da alamu ke nuni da cewa akwai yiyuwar a samu tarzomar nuna adawa da hakan akan titunan kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.