Lafiya
Mutane da ke kamuwa da hawan Jinni sun karu-Bincike
Wani Binciken masana kiwon lafiya ya bayyana cewar addadin mutane da ke kamuwa da Cutar hawan jinni ya ninka yadda aka saba gani musamman a kasashen da ke Asia da Afirka.
Wallafawa ranar:
Talla
Farfesa Majid Ezzati na Cibiyar koyar da aikin likita da ke London ya ce cutar ce ke haifar da shanyewar jiki da ciwon zuciya, kuma tana kashe akalla mutane miliyan 7 da rabi a kowacce shekara.
Rahotan da aka wallafa a Mujallar lafiya ta The Lancet ta ce tsakanin shekara 1975 zuwa 2015 an samu karuwar masu kamuwa da cutar a duniya daga miitan 594 zuwa biliyan 1 da miliyan 100.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu