Isa ga babban shafi

Iran ta zartas da hukuncin kisa kan mutum fiye da 300 a bana - Rahoto

Wata kungiya da ke gwagwarmayar kare hakkin dan adam a Iran ta ce mahukuntan kasar sun zartas da hukuncin kisa kan mutane fiye da 300 a bana kadai, adadin da ba’a ga makamancin sa ba tun 2015. 

Wasu mutane biyar da aka yankewa hukuncin kisa ta hanyar rataya a kasar Iran kenan, a birnin Mashhad ranar 01 ga Agustan 2007.
Wasu mutane biyar da aka yankewa hukuncin kisa ta hanyar rataya a kasar Iran kenan, a birnin Mashhad ranar 01 ga Agustan 2007. (Photo : AFP)
Talla

Kungiyar wadda ke da Ofishi a kasar Norway, ta ce daga farkon watan Janairu zuwa yau, an kashe mutane 307 ta hanyar rataya karin sama da mutane 75 kan yawan wadanda aka hallaka din a bara. 

Kungiyar ta kuma kara da cewa a watan Mayun da ya gabata kadai mahukuntan kasar sun rataye mutane 142, dalilin da ke kara jefa fargaba da razani a zukatan al’ummar kasar, yayin da hakkin dan adam ke fuskantar barzana. 

Wani rahoto da kungiyoyin kare hakkin dan Adam na IHR da ECPM suka fitar a farkon wannan shekara, ya nuna cewa mahukuntan Iran sun kara yawan mutanen da suke zartas wa da hukuncin kisa zuwa kashi 75 cikin 100 a shekarar 2022, matakin da masu kare hakkin na dan adam suka ce ana dauka domin tsorata masu zanga-zangar adawa da gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.