Isa ga babban shafi
Falasdinawa - Isra'ila

Martanin shugabannin duniya kan rikicin Isra'ila da Falasdinawa

Shugabannin kasashe da na hukumomin kasa da kasa na cigaba da jan hankali kan rikicin Isra’ila da Falasdinawa, inda wasu ke kiran da a kai zuciya nesa tare da taka tsan-tsan, wasu kuma na yin Alla-wadai da rikicin musamman da hare-haren jiragen yakin Isra'ila kan Falasdinawa a birnin Gaza da kuma makaman rokar da mayakan Hamas ke harbawa kan Isra'ilar.

Wasu Falasdinawa yayin ceto wata Dattijuwa daga wani gini da hare-haren jiragen yakin Isra'ila suka ragargaza a birnin Gaza.
Wasu Falasdinawa yayin ceto wata Dattijuwa daga wani gini da hare-haren jiragen yakin Isra'ila suka ragargaza a birnin Gaza. © AP - Khalil Hamra
Talla

Zuwa yanzu dai kimanin mutane 75 suka rasa rayukansu ciki har da Falasdinawa 69 da 'yan Isra'ila 6 a rikicin dake barazanar rikidewa zuwa kazamin yaki.

Antonio Guterres, Sakatary MDD
Antonio Guterres, Sakatary MDD MICHAEL TEWELDE AFP/File
Sakataren majalisar dinkin duniya Antonio Guterres ya bayyana damuwa kan yadda rikicin ke shafar wadanda basu jib a basu gani ba, inda yara kanana da mata ke rasa rayukansu dalilin luguden wutar jiragen yakin Isra’ila, zalika ya caccaki mayakan Falasdinawa kan harba rokokin da suke yi cikin Isra’ila kan fararen hula.
Wata Bafalasdiniya tare da 'ya'yanta bayan tserewa daga muhallinsu, don gujewa hare-haren jiragen yakin Isra'ila.
Wata Bafalasdiniya tare da 'ya'yanta bayan tserewa daga muhallinsu, don gujewa hare-haren jiragen yakin Isra'ila. AP - Khalil Hamra
A nata gefen fadar White House a Amurka cewa tayi, Isra’ila na da hujjar kare kanta daga hare-haren Hamas, to amma ya zama dole birnin Kudus ya kasance wajen zaman dukkanin Falasdinawa da ‘yan Isra’ila a lokaci guda.

Ita kuwa kungiyar tarayyar Turai EU A-wadai tayi da yadda Isra’ila ke korar Falasdinawa daga muhallansu, yayin da kuma ta ce ba za a lamunci hare-hare makaman rokar da Falasdinawa ke kaiwa fararen hula a Isra’ila ba, dan haka dole a kawo karshen rikicin.

Shugaban kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ta Arab League Ahmed Gheit
Shugaban kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ta Arab League Ahmed Gheit AP - Hussein Malla

Shugaban kungiyar hadin kan Larabawa ta Arab League Ahmed Gheit ya bayyana hare-haren jiragen yakin Isra’ila a matsayin tsantsar mugunta, tare da dorawa Isra’ilar alhakin barkewar rikicin na baya bayan nan, tare da kira ga hukumomin kasa da kasa su kawo karshen tashin hankalin.

Ita kuwa Turkiya cewa tayi ya dace gwamnatin Isra’ila ta gane cewar amfani da karfi ba zai murkushe ‘yancin neman hakkin Falasdinawa ba, yayin da shugaban Rasha Vladimir Putin ya bukaci dukkanin bangarorin biyu su tagaita wuta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.