Isa ga babban shafi
Somalia-Amurka

Sojan Amurka ya mutu a kasar Somalia

A Somalia daya daga cikin sojan Amurka na rundunar Africom ya rasa ran sa a wani gumurzu da ya wakana a daf da kan iyaka da kasar Kenya a lokacin da Sojan Somalia, Kenya hade da na Amurka suka kai samame a wata maboyar yan kungiyar Al Shebab.

Dakarun kasar Amurka a Somalia
Dakarun kasar Amurka a Somalia Kacper Pempel / Reuters
Talla

A shekara ta 2011 ne aka kori yan kungiyar Al Shebab daga birnin Mogadiscio, sai dai hakan bai rage musu kafi ba a kokarin su na wargaza zaman gwamnatin kasar dake samu goyan bayan kasashen Duniya.

An dai bayyana cewa hudu daga cikin dakarun Amurka sun samu munanan raunuka, takanas Shugaban Amurka Donald Trump ya aike da wasikar ta’azziya zuwa iyalan siojan da ya rasa ran sa a kasar ta Somalia.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.