Isa ga babban shafi
Syria-Amurka-Rasha

Mayakan IS sun sace mutane 2,000

Yan tawayen Syria dake samun goyon bayan kasashen yamma sun sanar da datse duk wata hanya da mayakan ISIL za su bi su ketara zuwa nahiyar turai. 

Mayakan Kurdawa yayin kaddamar da hari kan ISIL
Mayakan Kurdawa yayin kaddamar da hari kan ISIL Reuters
Talla

Lamarin na zuwa ne bayan da ‘yan tawayen Syrian da suka kunshi Kurdawa da larabawa suka bayyana cewa mayakan na ISIL sun sace mutane akalla 2,000 don yin garkuwa da su yayin da mayakan suka tsere daga arewacin birnin Manbij.

Mai Magana da yawun yan tawayen Sharfan Darwish ya ce yanzu haka sun kwace ikon yawancin yankunan birnin na Manbij daga hannun mayakan na IS.

Rahotanni sun ce an ga sama da motoci dari biyar makare da mutane na barin Birnin na Manbij zuwa Jarabulus da ke iyaka da Turkiyya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.