Isa ga babban shafi
Brazil

Yan Majalisan Dattawan Brazil sun tsige shugabar kasar Dilma Roussef

Yan Majalisar Dattawan Brazil 55 sun bayyana goyan bayan su na dakatar da shugabar kasar Dilma Rousseff bayan kwashe sa’oi 17 ana tafka mahawara.Majalisar bayan kada kuri'a ta amince da batun tsige shugabar kasar Dilma Roussef mai shekaru 68.Bangaren Uwargida Dilma Roussef sun bayyana cewa juyin mulki ne aka yiwa Dilma Roussef . 

Dilma Roussef  tsohuwar Shugabar kasar Brazil
Dilma Roussef tsohuwar Shugabar kasar Brazil AFP
Talla

Majalisar dattawan kasar bayan tafka mahawara kan shirin dakatar da shugabar kasar Dilma Rousseff saboda zargin da ake mata na almundahana da kuma cin hanci da rashawa ta amince da batun tsige ta,mataimakin Shugabar Michel Temer ne zai maye gurbin Uwargida Dilma na tsawon watanni shida.                                                .

 Michel Temer mai shekaru 75 ne zai jagoranci Brazil,tareda yi kokarin gani ya hada kawunan yan siyasa dama yaki da cin hanci da rashawa.

Bayan kamala shari’ar da za’ayi mata Majalisar zata nemi kuri’u biyu bisa uku dan tsige ta baki daya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.