Isa ga babban shafi
Syria

EU ta yaba da matakin gwamnatin Syria kan Madaya

Kungiyar tarayyar Turai ta yi marhaba da matakin gwamnatin Syria na amincewa da isar da kayayyakin jin-kai ga al-ummar garin Madaya da ke fama matsanacin yunwa yayin da ta bukaci a daina kai hare hare kan fararan hula a rikicin da ake yi a kasar.

Shugaban kasar Syria Bashar al- Assad
Shugaban kasar Syria Bashar al- Assad
Talla

Wannan na zuwa ne a dai dai lokacon da ake shirin gudanar da tattaunawar zaman lafiya tsakanin gwamnatin Syria da ‘yan tawaye a ranar 25 ga wannan watan da nufin kawo karshen rikicin kasar.

A cewar Federica Mogherini, shugabar harkokin wajen kungiyar tarayyar Turai, matakin da Assad ya dauka na a matsayin wani ci gaba dangane da samar wa al-ummar Madaya mafita daga matsancin halin da suka samu kansu a ciki saboda yakin Syria.

Yakin Syria dai ya yi sanadiyar mutuwar mutane dubu 250 a cikin shekaru biyar da suka gabata, lamarin da ya haifar da koma baya matuka ga kasar wadda a yanzu ta zama sansanin horar da masu tayar da kayar baya.

Bayanai dai sun tabbatar da cewa, mutane da dama ne ke mutuwa a dalilin yunwa a yankunan madaya da Foua da Kefraya, sai dai abin ya fi kamari a madaya wanda aka yi wa kawanya.

Kimanin mutane dubu 40 ne galibin su fararen hula ke zaune a madaya cikin yunwa da kishin ruwa, har ta kai suna cin kwari da ganyaryaki.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.