Isa ga babban shafi
Saudi Arabia

Saudiya na bincike kan al’amarin da ya auku a masallacin Makkah

Gwamnan birnin Makkah na Saudiya Yarima Khaled al-Fisal ya bada umarni gudanar da bincike kan ruftawar karafan fadada gini a Masallacin ka’aba a jiya Juma’a wanda ya yi ajali Mahajatta akalla 107.

Karafan Fadada Gini Masallacin Saudiya da ya rufta kan Mahajatta
Karafan Fadada Gini Masallacin Saudiya da ya rufta kan Mahajatta REUTERS/Mohamed Al Hwaity
Talla

A cewar hukumomin tsaron kasar yanzu haka akwai mutane kusan 238 da suka samu munanar raunin ka, kuma akwai yiyuwar samun karuwan adadin mamatan.

Wannan lamari ya kasance mumunar bala’i da ta auku kan Mahajjata tun bayan shekarar 2006 da daruruwan mahajatta suka rasa rayukansu sakamakon turmutsu-tsu.

Kawo yanzu dai ba a Fitar da bayanai kan  ‘yan kasar da hatsarin ya rutsa da su ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.