Tunisia
Birtaniya ta bukaci ‘yan kasarta su fice Tunisia
Biritaniya ta shawarci ‘yan kasarta da ke zaune a kasar Tunisia da su tattara su bar kasar, domin akwai alamun ana iya sake kai masu munanan hare hare a cikin kowane lokaci.
Wallafawa ranar:
Talla
Wannan gargadi na zuwa ne makwanni biyu bayan kazamin harin da aka kai kan masu yawon shakatawa yawancinsu Turawan Birtaniya a bakin ruwan Tunisia, inda aka kashe mutane 38.
Ana ganin Wannan mataki zai shafi tattalin arzikin kasar Tunisia wadda ta ke takama da samun makudan kudade daga ‘yan kasar Turai da ke zuwa yawon shakatawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu