Philippine
Yau Shugaban Philippine zai ziyarci yankunan da guguwa ta yi barna
A yau juma’a, Shugaban kasar Philippine, Benigno Aquino, ya ziyarci yankunan da mahaukaciyar guguwa ta afkawa, inda ya lashi takobin kawo karshen irin wannan bala’in a kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Kusan mutane 500 ne suka rasa rayukansu, sakamakon guguwar mai suna Bopha, da ta afkawa yankunan tsibrin Mindanao, da ke kudancin kasar, a ranar Talata da ta gabata.
Wasu daruruwan mutanen sun bata sakamakon guguwar, yayin da mutane fiye da dubu 300 suka rasa gidajensu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu