Ci gaba da Sauraren karar Karadzic a Hague
Shugaban Sabiyawan Bosnia, Radovan Karadzic zai nemi kare kansa a gaban kotun hukunta manyan laifuka a Yuguslavia a yau Talata. An cafke Karadzic a shekarar 2008 a Belgrade, saboda jagorantar rikcin Serbia day a yi sanadiyar mutuwar daruruwan mutane.
Wallafawa ranar:
Karadzic mai shekaru 67, ana tuhumarsa ne da aikata laifukan yaki tare da keta hakkin bil’adama da Dakarun Bosnia suka aikata a yakin da ya auku a shekarar 1992-95. Amma Karadzic ya musanta tuhume tuhumen da ake masa inda lauyan shi Peter Robinson ke cewa zai yi kokarin kare kansa.
Tuni dai Ratko Mladic ya gurfana a gaban Kotu da ake zargin ya jagoranci kisan kiyashin da aka yi wa Musulmi sama da 8,000 a yakin Bosnia.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu