Serbia
Kotun MDD ta fara sauraren karar Ratko Mladic
Kotun Hukunta mutanen da suka aikata laifukan yaki ta MDD dake zaman ta a Hague ta fara sauraron karar da aka kai na tsohon Kwamandan Sojan Serbia Ratko Mladic.A zaman kotun Ratko Mladic yaki amsa laifi inda ya nemi a bashir bayanan a rubuce domin yayi nazari tare da lauyan sa.Bayan wannan bukata sai Alkalin Kotun, Alphons Orie yace za a cigaba da tsare Mr. Mladic, a inda ake tsare wadanda ake tuhuma, kuma lauyan da aka bashi, Mr Aleksandar Aleksic, zai sa shi a hanya gameda sharuddan tsare shi.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: