Isa ga babban shafi
Serbia-ICC

Sauraren karar Kwamandan Serbia, Ratko Mladic a gaban kotu

Tsohon kwamandan Serbia, Janar Ratko Mladic, ya gurfana a gaban kotun Duniya a birnin Hague domin fuskantar zargi 11 na laifukan yaki da kisan kare dangi da keta hakkin bil’adama a yakin Bosnia a shekarar 1992-95.

Ratko Mladic a zauren kotun duniya lokacin sauraren karar shi a ranar 3 Yuni 2011.
Ratko Mladic a zauren kotun duniya lokacin sauraren karar shi a ranar 3 Yuni 2011.
Talla

Janar Mladic shi ne babban jami’I na karshe a yakin Balkan da zai gurfana a gaban kotun Duniya, saboda zargin kashe Musulmi yara maza da Manya sama da 7,000 a Srebrenica.

Sai dai Mladic wanda aka cafke a watan Mayun bara bayan kwashe shekaru 16 ana farautar shi, ya musanta zarge zargen da ake ma shi.

A cewar Mladic duniya ta san ko shi wanene a lokacin da aka fara sauraren karar shi a bara.

“ suna na Janar Ratko Mladic, ina kare mutane na da kasa ta, kuma yanzu zan kare kai na”, inji Mladic.

Wani hoton Bidiyo ya nuna Mladic cikin gungun Musulmi da suka kama a gidan yari.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.