Isa ga babban shafi

Ya zama wajibi Mali ta samar da mafita da shirya zabe- Kungiyar Tarayyar Afirka

Kungiyar Tarayyar Afirka a jiya Asabar ta bukaci kasar Mali da ta samar da mafita na dawo da kuma shirya mika mulki ga farraren fula ta hanyar shirya zabe.Kungiyar ta na mai cewa ana bukatar daukar matakin ne domin mayar da kasar kan tafarkin dimokuradiyya.

Rundunar sojin Mali ta ce ta dakile wasu jerin hare-haren ‘yan ta’addada suka kaisu kan wasu sansanonin jami'an tsaron kasar.
Rundunar sojin Mali ta ce ta dakile wasu jerin hare-haren ‘yan ta’addada suka kaisu kan wasu sansanonin jami'an tsaron kasar. REUTERS - PAUL LORGERIE
Talla

A farkon makon nan ne dai gwamnatin mulkin sojan kasar ta Mali ta bayar da umarnin dakatar da duk wasu harkokin siyasa, bisa la'akari da bukatar tabbatar da zaman lafiyar a fadin kasar ga baki daya.

MInistan harkokin wajen Mali Abdoulaye Diop yayin gaisa wa da wakilan mayakan Abzinawa bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiya dasu a ranar 1 ga watan Maris na shekarar 2015.
MInistan harkokin wajen Mali Abdoulaye Diop yayin gaisa wa da wakilan mayakan Abzinawa bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiya dasu a ranar 1 ga watan Maris na shekarar 2015. © Farouk Batiche, AFP file picture

al'ummar kasar na fatan zama lafiya,wannan ne babban aiki da majalisar sojin kasar ta saka  a gaba a cewar Firaministan kasar Mali Choguel Kokalla Maiga a lokacin da ya amsa wasu daga cikin tambayoyin manema labarai ganin ta yada ake shiga muhawara yan lokuta bayan da majalisar sojin kasar ta soke ayyujan jam’iyyun siyasa.

Babban birnin Bamako na kasar Mali
Babban birnin Bamako na kasar Mali Getty Images - john images

Kungiyar Tarayyar Afirka ta nuna matukar damuwarta kan matakin, tana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga dawowar mulkin dimokuradiyya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.