Isa ga babban shafi

Hukumomin sojin Mali sun haramtawa kafafen yada labarai yada labaran jam'iyyun siyasa

Hukumomin sojin Mali masu rike da madafan ikon wannan kasa a yau Alhamis sun haramtawa kafafen yada labarai buga duk wani labari kan ayyukan jam’iyyun siyasa na wannan kasar, kusan kwanaki daya da sanar da dakatar da wadanan jam’iyyu  daga ayukan su.

Shugaban Majalisar sojin Mali ,Kanal Assimi Goita
Shugaban Majalisar sojin Mali ,Kanal Assimi Goita © Colonel Assimi GOITA
Talla

A kasar ta Mali,vayan sanar da dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasa, babbar hukumar sadarwa ta kasa wato HAC a wata sanarwa ta ce “tana gayyatar dukkanin kafafen yada labarai kama daga rediyo, talabijin, jaridu da na yanar gizo da su dakatar da watsa shirye-shirye da suka jibanci ayyukan jam’iyyun siyasa na kasar da kungiyoyi masu aiki da su.

Dag cikin masu zanga-zanga a kasar Mali
Dag cikin masu zanga-zanga a kasar Mali © Florent Vergens / AFP

Babbar hukumar sadarwa ta kasa HAC ba ta bayar da karin haske ba a kan gidajen watsa labarai da za a iya baiwa damar fitar da irin wadanan labarai har idan hakan ta kasance a gaba.

Wadannan sabbin takunkumi ne kan duk wani furuci na adawa ko rashin amincewa da shugaban majalisar sojin kasar ta Mali ,wanda ya karbi mulki da karfi a watan Agustan 2020 ta hanyar hambarar da shugaban farar hula Ibrahim Boubacar Keïta.

Colonel Abdoulaye Maïga, Mali marabaajɛkulu ɲɛmaa.
Colonel Abdoulaye Maïga, Mali marabaajɛkulu ɲɛmaa. © Capture d'écran, journal ORTM

Wannan sabon salon na zuwa ne a dai dai lokacin da sojoji suka gaza a kan alkawarin da suka dauka, sakamakon matsin lamba daga kungiyar ECOWAS na mika wuya ga farar hula kafin ranar 26 ga Maris, 2024.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.