Isa ga babban shafi

Sai an daidaita yanayin tsaro gaba daya kafin a je zaben kasar Mali - Choguel

Firaministan kasar Mali Choguel Kokalla Maiga ya na mai bayyana cewa 'Gwamnatin mulkin sojin kasar za ta shirya zabuka ne kawai domin mika mulki ga farar hula da zarar an daidaita yanayin tsaro gaba daya.Mali na  karkashin mulkin sojoji ne tun bayan juyin mulkin da aka yi a baya-bayan nan a shekarar 2020 da 2021, inda matsalar tsaro ke kara ta'azzara daga kungiyoyin masu ikirarin da suka kama wasu yankunan kasar.

Choguel Maïga, Firaministan kasar Mali
Choguel Maïga, Firaministan kasar Mali AFP - MICHELE CATTANI
Talla

Firaminista Choguel Kokalla Maiga ya ce, "Dole ne matakin tabbatar da zaman lafiya ya kai matsayin da ba za a sake komawa gidan jiya ba, matakin da ya dace da samun damar shirya zabuka a wannan kasa.

Choguel Kokalla Maiga  na Magana ne a gidan talabijin na kasar da kuma aka watsa a kafofin sada zumunta da yammacin ranar Alhamis. .

Shugaban Majalisar Sojin Mali Kanal  Assimi Goïta.
Shugaban Majalisar Sojin Mali Kanal Assimi Goïta. © ORTM

Choguel Kokalla Maiga ne babban jami'i na farko da ya kawo Karin haske kusan kwana daya da yan siysa suka soma bayyana damuwa yan lokuta da majalisar sojin ta sanar da haramta ayyukan jam’iyyun siyasa a kasar ta Mali. Majalisar sojin kasar ta dau alkawalin mika mulki idan wa’din ya cika,sai ga shi ta kasa cika wannan alakwari  na ranar 26 ga Maris, 2024.

Firaministan kasar Mali Choguel K. Maiga
Firaministan kasar Mali Choguel K. Maiga © RFI/France24

Sakamakon matsin lamba daga kungiyar ECOWAS a yankin, gwamnatin mulkin soji kasar Mali ta yi alkawarin shirya zaben shugaban kasa a watan Fabrairu tare da mika mulki a karshen watan Maris, amma ta janyo suka a cikin gida bayan ta kasa yin hakan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.