Isa ga babban shafi

AU ta bukaci tashi tsaye wajen warware matsalar da ECOWAS ta shiga

Kungiyar Tarayyar Afirka AU ta bayyana matukar rashin jin dadi akan matakin da gwamnatocin sojin Burkina Faso da Mali da kuma Nijar suka dauka na ficewa daga cikin kungiyar ECOWAS ta yammacin nahiyar Afirka.

Shugaban hukumar gudanarwar kungiyar kasashen Afirka AU Moussa Faki Mahamat.
Shugaban hukumar gudanarwar kungiyar kasashen Afirka AU Moussa Faki Mahamat. AP - Ronald Zak
Talla

Cikin sanarwar da ta fitar, AU ta ce shugaban hukumar gudanarwarta Moussa Faki Mahamat, yayi kira ga shugabannin kasashen ECOWAS da su tashi tsaye wajen tattaunawa da kasashen uku da suka shelanta ficewa daga cikinsu.

A ranar Lahadin da ta gabata Nijar da Mali da kuma Burkina Faso, suka sanar da matakinsu na ficewa daga cikin ECOWAS, bayan shafe watanni ba tare da kyakkyawar alaka tsakaninsu da kungiyar ba, saboda juyin mulkin da sojoji suka yi a cikinsu.

A watan Yulin bara ne dai sojojin Nijar suka yi juyin Mulki, na Burkina Faso kuma a shekarar 2022, yayin na Mali suka kawar da gwamnatin farar hula a 2020.

Wannan ce kuma ta sa duk da cewar kasashen uku jiga-jigai ne wajen kafa ECOWAS a shekarar 1975, hakan bai hana kungiyar daukar matakin ladabtarwa na kakaba musu takunkumai ba, domin tilasta wa sojojin kasashen mayar da Mulki ga farar hula.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.