Isa ga babban shafi

Kenya: Shugaba Ruto ya gargadi jagoran 'yan adawa a kan tsaron kasa

Shugaban Kenya, William Ruto ya ce ba zai nemi amincewar abokin hamayyarsa a kan abin da ya shafi tsaron kasar ba, biyo bayan amincewa da zama a teburin tattaunawa da zummar kawo karshen mummunar zanga-zangar adawa da gwamnatinsa. 

Shugaban Kenya William Ruto.
Shugaban Kenya William Ruto. REUTERS - MONICAH MWANGI
Talla

 

Ruto ya ce zai rungumi tattaunawa, amma yana  mai gargadin abokin hamayarsa cewa ba zai lamunci wata zanga-zanga da za ta jefa rayuwa da kadarorin al’umma cikin hadari ba. 

Tun a watan Maris Jagoran ‘yan adawa, Raila Odinga  ya shirya zanga-zangar kwanaki 9 don nuna rashin amincewa da abin da ya kira gwamnati mara halasci, wadda ta jefa kasar cikin haali na matssin tattalin arziki. 

A ranar Asabar, bangaren gwamnati da na ‘yan adawa suka sanar da aniyarsu ta warware rikicin da ke tsakaninsu cikin ruwan sanyi, biyo bayan zanga-zangar da ‘yan adawa suka shirya, wadda  ta yi sanadin mutuwar mutane 20. 

Kasancewar Kenya  daya daga cikin kasashen da dimokaradiyya ta samu ginndin zama a nahiyar Afrika, tashin hankalin da kasar ta fuskanta ta  janyo kiraye-kirayen sasantawa  daga ciki da wajen kasar. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.