Isa ga babban shafi

'Yan sandan Kenya sun harba hayaki mai sa hawaye kan masu zanga-zanga

'Yan sandan Kenya sun harba hayaki mai sa hawaye kan tawagar madugun 'yan adawar kasar Raila Odinga a jiya Juma'a, ya yin da kungiyoyin kare hakkin dan adam suka yi tir da kamen da jami’an tsaro suka yi ba bisa ka'ida ba, a lokacin zanga-zangar adawa da gwamnati kan tsadar rayuwa da kuma karin harajin da ta yi.

'Yan sandan Kenya sun harba hayaki mai sa hawaye kan tawagar madugun 'yan adawar kasar Raila Odinga.
'Yan sandan Kenya sun harba hayaki mai sa hawaye kan tawagar madugun 'yan adawar kasar Raila Odinga. AP - Brian Inganga
Talla

A cewar wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa AFP, an harba hayaki mai sa hawaye kan ayarin motocin Odinga ne bayan da ya yi wa masu zanga-zangar jawabi a babban birnin kasar Nairobi.

'Yan sanda sun kuma dauki irin wannan mataki na tarwatsa masu zanga-zanga a birnin Mombasa da Kisumu.

Wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Faransa na AFP ya kuma bayyana cewa 'yan sanda sun yi kame a birnin Nairobi, inda aka tsaurara matakan tsaro a game da zanga-zangar da Odinga ya kira don nuna adawa da manufofin gwamnatin shugaba William Ruto.

A wajen gangamin, Odinga ya bayyana shirin tattara sa hannun mutane miliyan 10 a yunkurin tsige shugaba Ruto da ke zaman babban abokin hamayyarsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.