Isa ga babban shafi

Hadarin mota ya ritsa da mutane 24 a Zambia

A Zambia akalla mutane 24 da ke karkashin wata mujami’a suka rasa rayukan su sanadiyyar hadarin mota.

Babban asibiti birnin Lusaka a Zambia
Babban asibiti birnin Lusaka a Zambia DAWOOD SALIM / AFP
Talla

Hukumar yan Sanda da ta isa yankin mai suna  Chongwe da ke da nisan kilometa 42 da babban birnin kasar Lusaka a kan hanyar su ta zuwa lardin Siavonga mai nisan kilometa 195 da Lusaka,yan sanda sun bayyana cewa motar na dauke da mutane 35,motar ta yi tawo mu gama da wata babbar mota,inda nan take mutane  24 da suka hada da mata 23 da wani namiji suka rasa rayukan su a cewar kakkakin yan sanda Danny Mwale.

Wani yankin kasar Zambia daf da kan iyaka
Wani yankin kasar Zambia daf da kan iyaka AFP PHOTO / MARC JOURDIER

Kasar Zambia ta yi kaurin suna a fanin da ya shafi haduran mota sabili da rashin wadatatun hanyoyi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.