Isa ga babban shafi

Hakainde Hichlema, ya lashe zaben shugabancin Zambia

Dan takarar adawa a zaben shugabancin kasar Zambia Hakainde Hichlema, ya lashe zaben shugabancin kasar  da aka gudanar ranar alhamis da ta gabata kamar dai yadda alkalumman hukumar zabe suka nuna.

 Hakainde Hichilema Jagoran yan Adawa a kasar Zambia
Hakainde Hichilema Jagoran yan Adawa a kasar Zambia RODGER BOSCH AFP
Talla

Samarakon mazabu 155 daga cikin 156 da hukumar zaben ta fitar na nuni da cewa Hichilema ya samu kuri’u sama da milyan 2 da dubu 810 da kuri’u 757, yayin da shugaba mai-ci Edagar Lungu ya samu kuri milyan 1 da dubu 814 da 201 a wannan zabe.

Wani daga cikin magoya bayan jagoran yan Adawa
Wani daga cikin magoya bayan jagoran yan Adawa Patrick Meinhardt AFP

Lura da wadannan alkalumma ne shugaban hukumar zaben kasar Esau Chulu ya tabbatar da Hichileme a matsayin zababben shugaban kasar Zambia.

Dan shekaru 59 a duniya, Hichilema wanda shahrarren dan kasuwa ne, ya yi nasarar doke shugaban da ke kan karagar mulkin kasar ne bayan ya tsaya takarar har sau 6, kuma 3 daga cikinsu yana karawa da shugaba Lungu.

Shugaban kasar Zambia ,Edgar Lungu
Shugaban kasar Zambia ,Edgar Lungu REUTERS/Rogan Ward

A zaben da aka gudanar shekara ta 2016, duka duka an samu ratar kuri’u dubu dari daya ne a tsakanin mutanen biyu, sabanin wannan karo da aka samu tazarar kuri’u kusan milyan daya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.