Isa ga babban shafi

Najeriya ta aike da sojoji 197 don aikin wanzar da zaman lafiya a Gambia

Rundunar sojin Najeriya ta aike da dakarunta 197 Gambia domin gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya, daga cikinsu akwai manyan ofisoshi 14 da kuma sojoji 183.

Sojojin Najeriya a bakin aiki
Sojojin Najeriya a bakin aiki AFP - -
Talla

Wannan mataki na zuwa ne kwanaki 9 da tura wasu dakarun na daban zuwa kasar Guinea Bissau.

Dakarun wadanda tun a ranar 3 ga watan Afrilu suka soma horon shirin tafiya kasar a sansanin horas da masu aikin wanzar da zaman lafiya naMartin Luther Agwai International dake Jaji, a jihar Kaduna, sun shafe tsawon makonni 4 ana musu horo.

Yayin gabatar da jawabi ga dakarun na ECOWAS a lokacin da ake bikin kammala horon, Shugaban gudanarwar Taoreed Lagbaja ya ce aike dakarun ya kara nuna kudirin Najeriya a ayyukan tsaro da wanzar da zaman lafiya da ake gudanarwa a kasashen duniya.

Janar Lagbaja ya kuma bukaci dakarun su mayar da hankali wajen gudanar da aikin da ya kai su bil hakki a Gambia, tare da kaucewa duk wani abu da ka iya bata sunan rundunar sojin na Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.