Isa ga babban shafi

WHO za ta fara gwajin rigakafin cutar Ebola a Uganda

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce nan da makwanni za a fara gudanar da gwaje-gwaje kan allurar rigakafin cutar Ebola domin dakile yaduwar cutar wadda ta barke a kasar Uganda.

Likitoci kenan, lokacin da suke shiga cibiyar killace masu fama da cutar Ebola da ke Mubende, Uganda.
Likitoci kenan, lokacin da suke shiga cibiyar killace masu fama da cutar Ebola da ke Mubende, Uganda. AP - Hajarah Nalwadda
Talla

A watan da ya gabata ne Kampala ta sanar da samun mace-mace na farko a Uganda daga cutar mai saurin yaduwa, karon farko tun shekarar 2019, inda wata sanarwa da hukumar ta WHO ta fitar ta ce gwaji ya tabbatar da samun cutar a jikin mutum 54 da kuma mutuwar mutane 19.

Ministar lafiya ta kasar Uganda Jane Ruth Aceng ta shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa an samu mutuwar mutum guda a birnin Kampala bayan ya tsere daga tsakiyar gundumar Mubende inda aka fara samun bullar cutar.

A halin yanzu babu wani maganin rigakafin cutar Ebola nau’in Sudan da ke yaduwa a gabashin Afirka.

An dai fara samun bullar cutar ne ranar 20 ga watan Satumba, a yankuna biyar da suka hada da Mubende, a cewar WHO.

Wani bincike da hukumar lafiya ta duniya WHO ta gudanar ya gano cutar Ebola nau’in Sudan na barazanar yaduwa zuwa makwabtan kasashe saboda zirga-zirgar kan iyaka tsakanin Uganda da wasu kasashe.

Annobar mafi muni a yammacin Afirka ta auku ne tsakanin shekarar 2013 zuwa 2016 inda ta kashe mutane fiye da 11,300.

Uganda ta fuskanci bullar cutar Ebola da dama, na baya-bayan nan shine na shekarar 2019 inda akalla mutane biyar suka mutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.