Isa ga babban shafi

Libya na tafka hasarar dala miliyan 60 a kowace rana - Minista

Ministan man Libya Muhammed Aoun, ya ce kasarar na tafka hasarar dala miliyan 60 a kowacce rana sakamakon rufe cibiyoyin hakar danyen man kasar, a daidai lokacin da farashin gangarsa ta yi tashin gwauron zabi a duniya.

Matatar mai da ke garin Ras Lanuf da ke arewacin kasar Libya.
Matatar mai da ke garin Ras Lanuf da ke arewacin kasar Libya. AFP
Talla

Man fetur dai shi ne ginshikin tattalin arzikin kasar ta Libya da ke kokarin murmurewa daga rikicin tsawon shekaru 10, biyo bayan kifar da gwamnatin shugaba Moamer Kadhafi a wani boren da kungiyar tsaro ta NATO ta marawa baya a shekara ta 2011.

Sai dai tun a tsakiyar watan Afrilu rikicin siyasar Libya na baya bayan nan, ya gurgunta ayyukan manyan tashoshin jiragen ruwa guda biyu da kuma rijiyoyin mai da dama a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.