An gano wani kabari mai dauke da gawarwakin mutane 10 a Libya
Masu Bincike a kasar Libya sun gano wani kabari mai dauke da gawarwakin mutane 10 a Yankin da Yan Tawaye ke iko da shi a wajen binin Tripoli.
Wallafawa ranar:
Gwamnatin hadin kan kasar tace, 3 daga cikin gawarwakin an rufe fuskokin su kafin kashe su a Tarhuna dake da nisan kilimowa 80 daga babban birnin kasar.
Majalisar Dinkin Duniay ta bayyana matukar damuwa kan lokacin da aka gano irin wadannan kaburbura masu dauke da mutane da dama a watan Yunin bara bayan janyewar da dakarun Khalifa Haftar suka yi.
Kungiyar kare hakkin Bil Adama ta Human Rights Watch tace akalla mutane sama da 300 suka bata a Yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu