Isa ga babban shafi
Najeriya-Dubai

'Yan Najeriya 446 na daure a gidajen yarin Dubai- Gwamnati

Gwamnatin Najeriya ta ce yanzu haka 'yan kasar 446 na tsare a gidajen yarin kasar Hadaddiyar Daular Larabwa saboda aikata laifuffukan da ke da nasaba da safarar kwayoyi da kuma wasu laifuffuka.

Ko cikin watan jiya sai da aka kame wasu tarin 'yan Najeriya a Saudiya saboda aikata ba dai dai ba
Ko cikin watan jiya sai da aka kame wasu tarin 'yan Najeriya a Saudiya saboda aikata ba dai dai ba google.com
Talla

A jawaban da ya gabatar gaban taron 'yan Najeriya mazauna kasar ta Hadaddiyar Daular Larabawa, yayin wata ganawarsu da Shugaba Muhammadu Buhari a ziyarar da yanzu haka ya ke ci gaba da yi a kasar, Jakadan Najeriyar a birnin Dubai, Ambasada Mohammed Dansanta Rimi akwai tarin 'yan Najeriya da ke aikata ayyukan assha a kasar.

Kalaman na Ambasada Mohammed Dansamta Rimi na zuwa ne makwanni kalilan bayan kame wasu 'yan Najeriyar guda 5 da ake zargi da laifin fashi da makami a Kasar.

Ka zalika ko cikin watan jiya an yanke wasu tarin 'yan Najeriya hukuncin kisa wasu kuma daure a gidajen yarin Saudiya bayan samunsu da aikata ba dai dai ba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.