Kamaru na binciken zargin kisan fararen hula
Gwamnatin kasar Kamaru ta ce tana gudanar da bincike kan wani sabon faifan bidiyon da ke nuna jami’an tsaron ta na harbe akalla fararen hula 12 a yankin arewa Mai nisa da ake fama da matsalar boko haram.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kakakin gwamnati Issa Tchiroma Bakary ya ce gwamnati za ta gudanar da bincike duk da yake a baya an dade ana farfagandar bata mata suna kafin zaben shugaban kasar da za’ayi.
Kungiyar Amnesty International ta ce ta gudanar da bincike kan bidiyon da jin ba’asin shaidu da samun Karin bayanai ta tauraron dan adam da kuma nazarin makamai da kayan sojin da akayi amfani da su wadanda suka tabbatar mata cewar sojojin Kamaru ne.
Kungiyar ta ce an dauki hotan ne a kauyen Achigaya kafin watan Mayun bara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu