Najeriya bata fuskantar barazana daga mayakan ISIS
Shalkwatar tsaron Najeriya ta ce ba wasu kwararan hujjojin da ke tabbatar da cewa kasar na fuskantar barazana daga mayakan ISIS, bayan da wasu bayanai ke cewa yanzu haka kungiyar ta fara turo da baradenta zuwa Najeriya domin taya Boko Haram yaki da dakarun kasar.
Wallafawa ranar:
Sanarwar da mukaddashin daraktan yada labarai shalkwatar tsaron burgediya janar John Agim ya fitar a jiya laraba, ta ce ba wata hujjar da ke tabbatar da wannan ikirari.
Hukumomin Najeriya sun sanar da daukar matakan da suka dace tareda bayar da horo da ya dace zuwa sojojin kasar a yakin da suke yi da kungiyar Boko haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu