Isa ga babban shafi

An girke dubban 'yan sandan Jamhuriyar Congo a Kinshasa

Dubban jami’an ‘yan sandan Jamhuriyar Congo aka girke a sassan babban birnin kasar Kinshasa, a dai dai lokacin da a yau ‘yan adawa suka shirya gudanar da zanga-zangar tilastawa Joseph Kabila sauka daga shugabancin kasar.

Jami'an 'yan sandan Jamhuriyar Congo a gaban ginin kotun kolin kasar da ke birnin Kinshasa.
Jami'an 'yan sandan Jamhuriyar Congo a gaban ginin kotun kolin kasar da ke birnin Kinshasa. REUTERS/Finbarr O'Reilly
Talla

Limaman Cocin Katolika na kasar ne suka bukaci sake fita zanga-zangar duka da haramta ta da gwamnati ta yi, makwanni uku bayan da makamanciyar zanga-zangar ta juye zuwa tarzoma, inda akalla mutane 12 suka hallaka.

Kiran limaman Cocin, ya samu goyon bayan shugabancin mabiya addinin Islama da ke kasar, kamar yadda wakilinsu Shiekh Ali Mwinyi M’Kuu ya tabbatar.

Tun a jiya Asabar ‘yan sandan kasar suka kafa shingayen bincike a sassan birnin na Kinshasa, domin zakulo masu dauke da makamai, da kuma shirin dakile gudanar da zanga-zanar da gwamnatin Kabila ta haramta gudanar da ita.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.