Isa ga babban shafi
Kenya

‘Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga kan zabe a Kenya

‘Yan sanda a kasar Kenya sun yi amfani da hayaki mai sa kwalla domin tarwatsa magoya bayan jagoran ‘yan adawa Raila Odinga da ke gudanar da zanga-zangar neman a tube illahirin manyan jami’an hukumar zaben kasar.

‘Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga kan zabe a Kenya
‘Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga kan zabe a Kenya REUTERS/Baz Ratner
Talla

Dimbin magoya bayan Odinga ne suka yi cincirindo a gaban ginin hukumar zaben, a dai-dai lokacin da ya rage wata daya a sake gudanar da zaben shugabancin kasar kamar dai yadda kotun koli ta bukaci a yi.

Tun sauke zaben ake samun tashin hankali tsakanin magoya bayan shugaba Uhuru Kenyatta da ke alla-wadai da hukunci kotun da kuma magoya bayan Odinga da ke barazanar kauracewa zaben muddin ba a sauya shugabanni hukumar zaben kasar ba.

Kotun dai ta sauke zaben shugabancin kasar da aka gudanar 8 ga watan Agustan watan da ya gabata a kan kura-kuran da ta ce an tafka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.