Isa ga babban shafi
DR Congo

Mutane 11 suka mutu, Fursunoni 900 suka tsere a Janhuriyar Democradiya ta Congo

A kasar Janhuriyar Democradiya ta Congo mutane akalla 11 suka mutu, fursunoni fiye da 900 kuma suka tsere daga wani gidan yari dake gabashin kasar a lokacin da wasu 'yan bindiga suka kaiwa gidan yarin farmaki yau Lahadi.

Shugaban Janhuriyar Democradiya ta Congo Joseph Kabila
Shugaban Janhuriyar Democradiya ta Congo Joseph Kabila RFI
Talla

Gwamnan yankin Arewacin gunduman Kivu inda gidan yarin na garin Kangwayi yake, wato Julien Paluku ya shaidawa manema labarai cewa da rana tsaka ‘yan bindiga suka dirawwa gidan yarin.

A cewar shi a musayar wuta tsakanin ‘yan bindigan da jami'an tsaro dake gadin gidan yarin ne aka sami gawa 11 nan take.

A yanzu haka ya ce gidan yarin mai mutane 966, abinda suka rage basu wuce 30 ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.