Boko Haram ta kashe fararen hula 177 tsakanin 2015 zuwa 2016
Majalisar Dinkin Duniya ta ce tsakanin watan Fabarairun 2015 zuwa Sataumban 2016, kungiyar Boko Haram ta kashe fararen hula 177 a jihar Diffa da ke kudu maso gabashin Jamhuriyar Nijar.
Wallafawa ranar:
Rahoton da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a Yamai fadar gwamnatin Nijar ya ce akwai mutane akalla 13 da suka bata yayin da kungiyar Boko Haram ta sace hudu a yankin.
Mutane 101 an kashe su ne a yankin Bosso da ke bakin tafkin Chadi, sai 64 wadanda aka kashe a Diffa sannan wasu 12 a Nguimi.
Rahoton kuma ya ce adadin mutane 137 aka jikkata a hare haren na Boko Haram tsakanin 6 ga watan Fabrairun 2015 zuwa 30 ga SAtumban 2016.
Rahoton dai bai bayar da alkalumman adadin sojojin Nijar da aka kashe ba a hare haren na Boko Haram.
Alkalumman kuma ba su kunshi hare haren da Boko Haram ta kai ba a tsakanin watan Oktoban 2016 zuwa Janairun 2017.
Mayakan Boko Haram na Najeriya sun fara kaddamar da harin farko ne a ranar 6 ga watan Fabrairun 2015 a Nijar. Kuma tun daga lokacin suke kai hare hare a yankin Jihar Diffa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu